Isa ga babban shafi

Mutane 49 sun mutu a Kenya sanadiyar hadarin mota

Akalla mutane 49 ne suka mutu, a wani mummunar hadarin babbar motar dakon kaya da ke dauke da sundukai, a mahadar Londiani kusa da birnin Kericho, kamar yadda ministan sifirin kasar Kipchumba Murkomen, ya shaidawa manema labarai a yau Asabar.

Al'ummar yankin da aka samu hadarin motar da yayi sanadiyar mutuwar mutane 49 a Kenya ke nan ke tsare a inda lamarin ya faru.
Al'ummar yankin da aka samu hadarin motar da yayi sanadiyar mutuwar mutane 49 a Kenya ke nan ke tsare a inda lamarin ya faru. REUTERS - STRINGER
Talla

Babban jami’in ‘yan sandan yankin Geoffrey Mayek ya ce, kimanin wasu mutum 30 sun samu raunika, haka nan akwai wasu mutum biyu da ke makale ba’a ceto su ba.

Shugaban kasar William Ruto ya mika sakon ta’aziya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu.

Kenya na daya daga cikin kasashen Afrika da ke fama da matsalar hadarin mota, domin a cewar alkaluman da hukumar kare aukuwar hadura ta kasar ta fitar, sun nuna cewar a shekarar da ta gabata kadai mutane dubu 21 da dari 760 ne hadarin mota ya rutsa da su, daga cikin wancan adadi mutane dubu 4 da dari 690 suka mutu.

A wani rahoton da hukumar lafiya ta duniya WHO ta fitar a watan Satumbar shekarar da ta gabata, ya ce nahiyar Afrika ce ke kan gaba wajen aukuwar hadara a duniya, inda mutane sama da dari 8 ke mutuwa a kowace rana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.