Isa ga babban shafi

Majalisar dokokin Libya ta zargi gwamnati da yunkurin kashe dan majalisa

Majalisar dokokin Libiya da ke gabacin kasar ta zargi gwamnatin kasar mai hedkwata a Tripoli da kai hari gidan daya daga cikin ‘yan majalisarta ta hanyar amfani da jirgin yaki mara matuki.

'Yan tawayen Libya a shekarar 2015.
'Yan tawayen Libya a shekarar 2015. ASSOCIATED PRESS - Hussein Malla
Talla

Sai dai da take sanar da matakin, gwamnatin hadin kan kasa da Majalisar Dinkin Duniya ta amince da ita a Libya, ta ce hare-haren sun shafi maboyar wasu gungun masu fasa kwaurin man fetir da kwayoyi da kuma mutane ne a kewayen Zawiya da ke gabar tekun Bahar Rum a yammacin babban birnin kasar.

Ta ce harin bisa umurnin Firanministan rikon kwarya Abdulhamid Dbeibah ya yi nasara a kan wadandan bata gari.

Sai dai majalisar da ke da mazauni a gabashin kasar, ta ce harin da aka kai an kai shi ne gidan dan majalisar Zawiya Ali Bouzribah, mai adawa da gwamnatin Dbeibah.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.