Isa ga babban shafi

An tsawaita dokar ta baci da aka sanya a yankunan Burkina-Faso

Burkina Faso, kasar da ke fama da matsalar ‘yan ta’adda masu ikirarin jihadi ta sanar da tsawaita dokar-ta-baci da da ta kakaba a kan yankuna 13 na kasar da karin watanni 6 tun a daga karshen watan Maris.

Taswirar Burkina Faso da ke fama dfa rikicin 'yan ta'adda masu ikirarin jihadi.
Taswirar Burkina Faso da ke fama dfa rikicin 'yan ta'adda masu ikirarin jihadi. © RFI
Talla

Minstar shari’ar kasar,  Bibata Nebie Ouedraogo ta ce gwamnati ta dau wannan mataki ne don jaddada nasararta a yakin da take da ta’addanci.

Gwamnatin kasar ta sanya dokar ta baci a yankunan da da rikicin ta’addanci ya fi shafa  ne tun a watan Maris na shekarar da ta gabata.

Burina Faso, wadda sojoji suka kwace ragamar mulkinta a shekarar 2022 tana fama da matsalar ‘yan ta’addda masu ikirarin jihadi da ke shiga kasar daga Mali tun daga shekarar 2015.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.