Isa ga babban shafi

Wani harin ta'addanci ya hallaka sojojin Burkina Faso da dama

Gwamnatin mulkin sojin Burkina Faso tace akalla sojinta 33 suka gamu da ajalinsu yayin da wasu 12 suka jikkata samakon wani kazamin kari da aka kai wani sansanin sojinta a gabashin kasar ranar Alhamis.

Wasu dakarun Burkina Faso ke sintiri da babura a wasu kauyukan arewacin kasar. 10/11/2019
Wasu dakarun Burkina Faso ke sintiri da babura a wasu kauyukan arewacin kasar. 10/11/2019 © MICHELE CATTANI/AFP
Talla

Harin da aka kai a safiyar ranar Alhamis ya auna sansanin sojojin da ke Ougarou, a yankin gabashin Burkina Faso.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar ta ce sojojin da aka yi wa kawanya sun kashe ‘yan ta’adda akalla 40 kafin a kai musu dauki.

Karuwar hare-hare

Burkina Faso dai na daya daga cikin kasashen yammacin Afrika da dama da ke fama da tashe tashen hankulan masu kaifin kishin Islama da suka barke daga makwabciyar kasar Mali cikin shekaru goma da suka gabata, inda suka kashe dubban mutane tare da raba sama da miliyan biyu da muhallansu.

Tashe-tashen hankula a kasar sun yi kamari a 'yan watannin da suka gabata yayin da hukumomi ke kokarin dawo da martabar kasar duk da karfafa ayyukan tsaro.

Mutuwar sama da mutane 150

Ko a makon jiya wasu mutane sanye da kayan sojoji sun kashe akalla mutane 150 a wani samame da suka kai a wani kauye da ke arewacin Burkina Faso, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.