Dan sandan Tunisiya ya kashe masu ibadar Yahudawa da jami'an tsaro
Akalla masu Ibadan shekara shekara na yahudawa biyu da ‘yan sanda biyu aka kashe a wata shahararriyar mujami'ar kasar Tunisiya a ranar Talata a wani hari da wani dan sanda ya kai.
Wallafawa ranar:
Ma'aikatar harkokin cikin gidan Tunisiya ta ce wasu mutane hudu da suka ziyarci mujami'ar Ghriba da ke tsibirin Djerba tare da wasu jami'an tsaro biyar sun jikkata a harin kafin a kashe maharin.
A cikin wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen Tunisiya ta fitar ta bayyana masu Ibadan biyu da aka kashe amatsayin daya dan kasar Tunusiya ne mai shekaru 30 da kuma Ba-Faranshe mai shekaru 42, sai dai ba a bayyana sunayensu ba.
An kai harin ne bayan da maharin ya fara harbin wani abokin aikinsa tare da daukar harsashi kamar yadda ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar ta sanar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu