Isa ga babban shafi

AU ta yi kira da a taimaka wa fararen hula da ke tserewa rikicin Sudan

Kungiyar Tarayyar Afirka ta yi kira ga makwabtan Sudan da kasashen duniya da su taimaka wa mutanen da ke gujewa mummunan fadan da ake gwabzawa a can tare da sabunta kiran tsagaita bude wuta.

Wasu mazauna Sudan yayin kokarin ficewa daga kasar don gujewa fadan da ake gwabzawa tsakanin rundunonin dakarun kasar biyu.
Wasu mazauna Sudan yayin kokarin ficewa daga kasar don gujewa fadan da ake gwabzawa tsakanin rundunonin dakarun kasar biyu. REUTERS - EL TAYEB SIDDIG
Talla

Cikin wata sanarwa ofishin Shugaban hukumar ta AU Moussa Faki Mahamat ya ce  suna ci gaba da sanya ido tare da nuna matukar damuwa game da halin da fararen hula ke ciki a rikicin kasar Sudan.

Faki ya kuma yi kira ga sojojin Sudan da dakarun sa kai na RSF da su gaggauta amincewa da tsagaita bude wuta na dindindin domin saukaka kai agajin jin kai ga mutanen Sudan da ke cikin tsananin bukata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.