Isa ga babban shafi

Sojojin Burkina Faso sun ceto Mata 66 da 'yan ta'adda suka sace

Mahukuntan Burkina Faso sun sanar da nasarar ceto Mata da kananan yara 66 wadanda ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su cikin makon jiya a arewacin kasar.

Wasu Sojojin Burkina Faso.
Wasu Sojojin Burkina Faso. AFP - SIA KAMBOU
Talla

Sanarwar nasarar ceto Matan 62 da kananan yara 4 da aka bayyana ta gidajen talabijin din kasar sun ce dakarun Sojin kasar ne suka ja tunda da ‘yan ta’addan tare da gwabza fada gabanin ceto fararen hular a jiya juma’a.

Sa’o’I kalilan bayan sace matan ne tawaga ta musamman daga rundunar Sojin kasar ta bazama dazuka don kwato daga hannun ‘yan ta’addan wadanda ke kaddamar da mabanbantan hare-hare a sassan kasar musamman arewaci tare da kisan tarin fararen hula da sunan jihadi.

Gidajen talabijin yayin labaransu na daren jiya juma’a sun rika nuna hotunan matan 62 da yara 4 wadanda aka dawo da su birnin Ougadougou.

A ranakun alhamis da juma’a na makon jiya ne ‘yan ta’addan suka sace matan a yankin Arbinda na arewacin kasar lokacin da suke kan hanyarsu ta neman abinci ga iyalansu.

Wasu rahotanni sun ce an yi nasarar ceto matan ne a yankin Tougouri da ke gab da tsakiyar kasar tazarar kilomita 200 da kudanci gabanin a dakkosu a jirgi zuwa birnin Ougadougou don ganawa da shugabancin Sojin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.