Isa ga babban shafi

Gwamnatin Habasha na fatan warware rikicin arewacin kasar da yan tawaye

Manzon Amurka a yankin Afirka Mike Hammer, ya gana da mataimakin firaministan kasar Habasha Demeke Mekonnen a birnin Addis Ababa a jiya Juma'a, a kokarinsa na kawo karshen rikici a arewacin kasar.

Daya daga cikin yan tawayen Habasha
Daya daga cikin yan tawayen Habasha AFP - AMANUEL SILESHI
Talla

Bayan wata ziyara da ya kai a watan Satumba na shekarar nan, Mike Hammer ya koma yankin tun ranar 3 ga watan Oktoba, da fatan ganin an  dakatar da tashin hankali a arewacin Habasha nan take da kuma goyon bayan kaddamar da tattaunawar zaman lafiya a karkashin kungiyar Tarayyar Afirka ta  AU, a cewar ma'aikatar harkokin wajen Amurka.

A farkon watan Oktoba ne gwamnatin tarayya ta Firaminista Abiy Ahmed da wakilan ‘yan tawaye a yankin Tigray suka ce a shirye suke su je tattaunawar da kungiyar kasashen afirka ta AU ta gayyace su a Afirka ta Kudu.

Sai dai ba a iya gudanar da wannan tattaunawa ba, musamman saboda matsalolin kungiyoyi da na kayan aiki, a cewar jami'an diflomasiyya.

A ranar Juma’a, yayin tattaunawa da  Hammer,  firaministan kasar Habasha Demeke wanda kuma shi ne ministan harkokin wajen kasar, ya ​​jaddada aniyar gwamnati na ganin an warware rikicin arewacin kasar cikin lumana”, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar ta wallafa a shafinta na twitter.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.