Isa ga babban shafi

'Yan tawayen Tigray sun yi barazanar watsi da yarjejeniyar tsagaita wuta

Kwamandan 'yan tawayen yankin Tigray da ke arewacin Habasha ya sha alwashin cewa za su ci gaba da fafatawa da dakarun gwamnati har sai an cika  sharuddan da suka gindaya na tsagaita wuta.

Wasu 'yan tawayen yankin Tigray na Habasha.
Wasu 'yan tawayen yankin Tigray na Habasha. © AP Photo/Ben Curtis
Talla

Janar Tsadkan Gebretensae ya ce burinsu shi ne tilastawa gwamnatin Habasha janye shingen da ta sanya a yankin tare da amincewa da a warware rikicin da ke tsakaninsu a siyasance.

Gwamnati dai ta musanta ikirarin ‘yan tawayen na cewa dakarunta sun yi wa yankin na Tigrai kawanya gami da hana shiga ko fita daga cikinsa, kana kuma ta yi watsi da batun tattaunawar sulhun.

Rayukan dubban mutane ne dai suka salwanta tun bayan barkewar yaki a yankin Tigray cikin watan Nuwamban bara waccan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.