Isa ga babban shafi

Habasha ta tsaurara matakan tsaro a kan kayan agaji na yankin Tigray

Kasar Habasha ta bukaci tsaurara matakan tsaro akan kayan agajin da ake kaiwa yankin Tigray saboda zargin da take yiwa kungiyoyin agaji da kai wasu kayayyakin da aka haramta zuwa hannun Yan Tawaye.

Wata mata goye da danta yayin bin layin karbar tallafin abinci a sansanin 'yan gudun hijira na wadanda rikicin Tigray ya raba da muhallansu a garin Shire da ke yankin na Tigray.
Wata mata goye da danta yayin bin layin karbar tallafin abinci a sansanin 'yan gudun hijira na wadanda rikicin Tigray ya raba da muhallansu a garin Shire da ke yankin na Tigray. © REUTERS/Baz Ratner/File Photo
Talla

Mataimakin Firaministan kasar Demeke Mekonen yace ya zama wajibi jami’an tsaro sun sanya ido sosai domin ganin cewar ba’a baiwa Yan Tawayen TPLF kayayakin da aka haramta ba.

Wasu kauyawa yayin komawa gidajensu daga cin kasuwa a garin Yechila da ke kudu maso tsakiyar yankin Tigray mai fama da rikici. 10 ga Yuli, 2021.
Wasu kauyawa yayin komawa gidajensu daga cin kasuwa a garin Yechila da ke kudu maso tsakiyar yankin Tigray mai fama da rikici. 10 ga Yuli, 2021. © REUTERS/Giulia Paravicini

Mekonen yace ya gano cewar ana safarar man fetur fiye da yadda aka amince zuwa yankin tare wasu kayayyakin da aka haramta wadanda Yan tawayen ke amfani da shi wajen kai hari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.