Isa ga babban shafi
Rikicin Tigray

Sojojin Habasha sun kona wani dan kabilar Tigrai da ransa

Hukumar Kare Hakkin dan Adam ta kasar Habasha ta ce dakarun gwamnati ne suka kone wani dan kabilar Tigray da ransa har lahira, cikin wani faifan bidiyo da ya yadu ta shafukan sada zumunta, abinda ya janyo cece-kuce a ciki da wajen kasar.

Wani wuri a yammacin yankin Tigray mai fama da rikici da ke kusa da garin Humera.
Wani wuri a yammacin yankin Tigray mai fama da rikici da ke kusa da garin Humera. © REUTERS/Baz Ratner
Talla

A ranar Asabar ne gwamnatin Habasha ta sha alwashin gudanar da bincike tare da daukar mataki kan duk wanda ke da hannu a cikin ta’addancin, wanda faifan bidiyon da aka yada ya nuna yadda wasu mutane da suka hada da masu sanye da kakin soji ke yi wa mutumin da aka kashe ba'a, kafin daga bisani su cinna masa wuta.

Wannan danyen aikin ya afku ne a ranar 3 ga watan Maris da muke, a yankin Benishangul Gumuz da ke arewa maso yammacin kasar mai iyaka da Sudan da Sudan ta Kudu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.