Isa ga babban shafi

Zanga-zangar adawa da kasancewar dakarun Faransa Burkina faso

A Ouagadougou babbam birnin kasar Burkina Faso, jama’a sun gudanar da zanga-zangar adawa da kasancewar dakarun Faransa wannan kasa a jiya asabar.

Wasu daga cikin masu  goyon bayan majalisar sojin Burkina Faso
Wasu daga cikin masu goyon bayan majalisar sojin Burkina Faso © OLYMPIA DE MAISMONT / AFP
Talla

Masu zanga-zangar lumana dauke da aluna  sun  taru a wurin nan  mai dauke da sunan tsohon Shugaban sojin kasar Thomas Sankara da aka hallaka  a shekara ta 1987 bayan wani juyin mulki da Blaise Compaore ya kitsa.

Masu zanga-zangar sun gayyaci daukacin yan kasar masu rajin kare Burkina Faso da son dawo da zaman lafiya a kasar na ganin sun sake fitowa ranar 12 ga watan Agusta a wani gaggarumin gangami da zai gudana birnin na Ouagadougou  da nufin cewa Faransa da dakarun ta su fice daga wannan kasa kamar dai yadda Mali ta yi a baya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.