Isa ga babban shafi

Mata na taimakawa kungiyoyin yan ta'adda a Burkina Faso

Hukumomin Burkina Faso a jiya juma’a sun  bayyana damuwa da takaici ganin ta yada ake samun mata dake dafawa mayakan jihadi a hare-haren da suke kai cikin kasar.

Tawagar Shugaban kasar kanal  Paul-Henri Damiba, tare da rakiyyar jami'an gwamnatin sojin burkina Faso a Dori
Tawagar Shugaban kasar kanal Paul-Henri Damiba, tare da rakiyyar jami'an gwamnatin sojin burkina Faso a Dori via REUTERS - BURKINA FASO'S PRESIDENTIAL PRES
Talla

Minista kula da  jinsi da iyalin  na kasar ta Nurkina Faso Salimata Nebie ce ta sanar da haka yayin wani taron  manema labarai.

Jami’ar gwamnatin ta bayyana cewa kasancewar mata da kungiyoyin yan ta’adda a wannan lokaci,na daf da zama  ruwan dare a wani lokaci da hukumomi ke iya kokarin su don ganin an magance matsallar ta’addanci da rashi tsaro a fadin kasar ta Burkina Faso.

A karshe Ministar ta bayyana cewa biyo bayan harin ta’addanci da wasu tsageru suka kai wa ayarin sojin kasar ranar 25 ga wannan watan da muke cikin sa  a yankin Kelbo dake arewacin kasar , an hango mata na kwashe gawarwakin mayankan jihadi tareda kai dauki ga wandada suka jikata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.