Isa ga babban shafi

Burkina Faso: Zaman makoki na kwanaki 3 bayan harin ta'addanci

Akalla mutane 79 ne ‘yan ta’adda suka kashe a Seytenga  dake arewacin Burkina Faso, al’amari mafi muni tun bayan juyin mulkin da aka yi a kasar, kamar yadda kakakin gwamnatin kasar Lionel Bilgo ya bayyana a  jiya Litinin.

Daya daga cikin yankunan Burkina Faso dake fama da rashin tsaro
Daya daga cikin yankunan Burkina Faso dake fama da rashin tsaro AP - Sam Mednick
Talla

Bilgo ya ce ya zuwa yanzu sojoji sun gano gawarwaki 79 bayan da aka kai hari a kauyen Seytenga a cikin daren Asabar, inda ya kara da cewa adadin na iya karuwa.

Ya shaida a wani taron manema labarai cewa ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa da su sun koma kauyen, k,um aba mamaki sun tafi da wasu gawarwaki.

A garin Seytenga ne aka yi mummunan bata kashi a makon da ya gabata, inda aka samu sarar rayuka.

An kashe jandarmomi 11 a ranar Alhamis a wannan gari, lamarin da ya wajabta wani sintirin soji da ya yi sandin mutuwar mayaka masu ikirarin jihadi guda 40.

Kungiyoyin agaji a yaankin sun ce kimanin mutane dubu 3 ne aka bai wa mafaka a garuruwan da ke makwaftaka da kauyen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.