Jama'a sun fusata a arewacin Burkina Faso sabili da rashin tsaro
Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zanga lumana jiya asabar a garin Pama dake lardin Kompienga dake gabashin kasar Burkia Faso da nufin nuna takaici da damuwar su ganin ta yada mahara ke ci gaba da afkawa mazauna wadanan yankuna.
Wallafawa ranar:
Masu zanga-zangar sun samu goyan bayan shugabanin addinai,Sarakunan gargajiya, kungiyoyin farraren hula ,suka kuma yi amfani da wannan dama tareda rubuta wasika ga babban jami’in gwamnati na yankin don nuna masa rashin ko in kula da majalisar soji ke yi dangane da batun tsaro a wannan yaki da yan ta’adda.
Burkina Faso da wasu kasashen yankin Sahel na fama da wannan matsala ta yan ta'adda,al'amarin da ya durkusar da lamuran da suka shafi tattalin arziki,kasuwanci.ilimi da kiwon lafiya ga baki daya.
A wasu yankunan kasar ta Burkina Faso musaman arewacin kasar,sheidu sun tabbatr da cewa jami’an tsaro sun bar wurare ga baki daya ga hannun yan bindiga.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu