Adadin wadanda suka mutu a rikicin kabilancin Sudan ya kai 60
Rikicin kabilanci dan aka yi a yankin kudancin jihar Blue Nile a kusa da iyakar Sudan da Habasha, ya yi sanadin mutuwar mutane 60 tare da jikkata 163 ya zuwa yanzu, a cewar ma’aikatar lafiyar sudan din.
Wallafawa ranar:
Kamfanin dillancin labarn Faransa ya ruwaito cewa 13 daga cikin wadanda suka jikkata suna cikin halin rai kwakwai-mutu-kwakwai, kuma za a garzaya da su zuwa asibitoci a birnin Khartoum.
A ranar Asabar ce hukumomi suka ayyana dokar hana fitar dare a yankuna da ake gwabza rikicin kabilancin tsakanin wasu kabilu 2.
An kona shaguna 16 tun bayan tashin rikicin da ya kunno kai sakamakon takaddama a kan filaye tsakani kabilar Berti da Hausawa a ranar Litinin da ta gabata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu