Isa ga babban shafi

Mutane biyar aka kashe a Sudan yayin zanga-zangar neman kawo karshen Gwamnatin soji

Akalla mutane biyar ne aka kashe a Sudan a lokacin da sojoji ke kokarin tarwatsa masu zanga-zangar neman kawo karshen mulkin sojoji a kasar a birnin Kharthoum.

Zanga-zangar kyamar Gwamnatin Sojin Sudan
Zanga-zangar kyamar Gwamnatin Sojin Sudan REUTERS - MOHAMED NURELDIN ABDALLAH
Talla

Kamfanin dillancin labarai na Faransa AFP ya ruwaito cewar jami’an tsaro sun harba hayaki mai sa hawaye don tarwatsa daruruwan masu zanga-zangar, wacce itace ta baya-bayan nan da aka gudanar don nuna rashin gamsuwa da mulki sojoji a kasar cikin watanni 8.

Wasu daga cikin masu zanga-zanga a kasar Sudan
Wasu daga cikin masu zanga-zanga a kasar Sudan © Marwan Ali / AP

 

Jami’an kiwon lafiya sun ce mutane biyu daga cikin wancan adadin sun mutune ta sanadiyar harbi kai tsaye a kirjin su, lamarin da ya sa adadin masu zanga-zangar da aka kashe a cikin watanni ya kai dari da biyar.

Kamfanin dillancin labaran na AFP ya kuma ruwaito cewar, an katse internet da kuma layukan waya a safiyar alhamis din nan, a wani mataki da hukumomin Sudan ke amfani da shi wajen hana fitowar mutane da dama wajen zanga-zanagr.

An kuma tsaurara matakan tsaro a Khartom duk da dage dokar tabaci da aka sanya a birnin bayan gudanar da juyin mulki, inda sojoji da ‘yan sanda suka rufe duk wasu hanyoyi da ke zuwa shalkwatar sojoji da kuma fadar shugaban kasar.

Jakadan majalisar dinkin duniya a kasar Volker Perthes da kuma ofishin jakadancin Amurka, sun bukaci a takaita rikicin da kuma baiwa fararen hula kariya don gudun rasa rayuka.

Sudan dai ta shiga cikin rudani ne ta hanyar zanga-zanga, bayan da tattalin arzikin kasar ya tabarbare a karkashin jagorancin Burhan da ya kwace mulki a shekarar da ta gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.