Isa ga babban shafi

An bukaci Sudan ta gagguta bincike kan kisan masu zanga-zanga

Wani jami’in hukumar kare hakin dan adam ta majalisar dinkin duniya ya yi kira ga hukumomin Sudan da su gaggauta bincike a kan kisan masu zanga zang da sauran manyan laifuka da ake aikatawa a kasar, a daidai lokacin da adadin  mutanen da aka kashe tun da sojoji suka karbe mulki a shekarar da ta gabata ya kai 100.

Wasu masu zanga zanga a birnin Khartoum na Sudan.
Wasu masu zanga zanga a birnin Khartoum na Sudan. AFP - EBRAHIM HAMID
Talla

Adam Dieng ya shaida wa manema labarai cewa abin takaici ne ganin yadda mutane kusan dari suka mutu, sama da dubu 5 suka jikkata sakamakon amfani da karfi fiye da kima da jami’an tsaron kasar ke yi a kan fararen hula.

Sudan ta fada cikin tashin hankali tun bayan juyin mulki, ga kuma dirar mikiya a kan masu zanga zanga da sojoji ke yi tun lokcin da kwamndan sojin kasar  Abdel Fattah al-Burhan  ya sanar da kwace gwamnatin kasar a ranar 25 ga watan Oktoba, lamarin da ya ya kawo tsaiko a kokarin da ake na mika mulki ga fara hula.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.