Isa ga babban shafi

Mutum daya ya mutu bayan sabunta zanga-zangar adawa da sojoji a Sudan

Jami'an tsaron Sudan sun kashe mutum guda a jiya Asabar, yayin zanga-zangar da aka sabunta  ta adawa da mulkin sojojin kasar sojoji, wadanda juyin mulkin da suka yi ya kawo cikas ga shirin sake mika jagorancin kasar ga farar hula a shekarar bara.

Masu zanga-zanga a Sudan.
Masu zanga-zanga a Sudan. AP - Marwan Ali
Talla

Wata sanarwa da kwamitin likitocin sudan ya fitar, ta ce  mutumin da ba a tantance ba, ya mutu ne sakamakon harbinsa da aka yi da harsashi a kirji, yayin zanga-zangar adawa da sojojin a birnin Omdurman.

Mutuwar ta baya-bayan nan dai ta sanya jumillar adadin mutanen da suka mutu a zanga-zangar Sudan kaiwa 96, tun bayan juyin mulkin da sojojin kasar suka yi a ranar 25 ga watan Oktoba karkashin jagorancin babban hafsan soji Abdel Fattah al-Burhan.

Kimanin mutane 100 ne suka jikkata ranar Alhamis da ta gabata kadai, yayin zanga-zangar adawa da mulkin sojojin Sudan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.