Isa ga babban shafi

An kashe sama da mutane 200 a rikicin kabilanci a Sudan

Akalla mutane 213  ne aka kashe a rikicin da aka kwashe kwanaki 3 ana yi tsakanin Larabawa da sauran kabilu a yammacin yankin Darfur na Sudan.

Wata kungiyar 'yan tawaye  a Sudan
Wata kungiyar 'yan tawaye a Sudan (Photo : AFP)
Talla

Yammacin yankin Darfur ya tsunduma cikin rikici da aka kwashe kwanaki ana gwabzawa a Krink, wani kauye mai yawan mutane kusan dubu  500, inda aka fi samun ‘yan kabilar Massalit, kuma gwamnan jihar Khamees Abkar ya tabbatar da yawan mutanen da suka suka mutu a wani faifen bidiyo.

A ranar Juma’a da ta gabata ne rikici ya fara barkewa, ya kuma ta’azzara a lokacin da wasu, dauke da makamai suka afka wa kauyukan wadanda ba Larabawa ba a matsayin ramuwar gayya  ga kisan wasu mutanensu biyu da aka yi.

A ranar Talata, kungiyar likitoci ta kasa da kasa ta Medecins Sans Frontiere ta ce an kashe ma’aikatan lafiya da dama a rikicin saboda hare hare da aka kai wa asibitoci.

Rikicin Darfur da aka fara a shekarar 2003, yayi sanadin  mutuwar sama da mutane dubu 300 tare da daidaita miliyan 2 da rabi a cewar majalisar dinkin duniya.

Wannan  rikici na baya bayan nan na zuwa ne a daidai lokacin da Sudan ke kokarin girgijewa daga matsalar da juyin mulki da jagoran soji, Abdel Fattah al-Burham ya jagoranta a watan Oktoban 2021.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.