Isa ga babban shafi

Dakarun Somalia na boye sun bayyana a Eritrea

Dakarun Somalia dake karbar horon aikin soji a Eritrea sun fito bainar jama’a a karon farko, shekaru uku bayan da aka fara cece-kuce game da daukarsu aiki.

Sojojin kasar Somalia.
Sojojin kasar Somalia. AP - Farah Abdi Warsameh
Talla

Hoton farko na sojojin Somalian da ya bayyana, yana nuna su ne yayin faretin da suka yi a ranar Asabar, yayin karbar bakuncin sabon shugaban kasarsu Hassan Sheikh Mohamud, wanda ke ziyarar kwanaki hudu a Eritrea.

Mohamud ya ziraci sabbin dakarun nasa ne tare da takwaransa ba Eritea Isias Afawerki a birnin Asmara domin tattaunawa da takwaransa.

Bayanai sun ce tsohon shugaban kasar Somalia Muhd Abdul Farmajo ne ya dauki dakarun kimanin dubu 5 tare da tura su Eritrea don samun horo.

Sai dai matakin ya zamewa tsohon shugaba Farmajo kadangaren bakin tulu, bayan da 'yan adawa suka rika caccaka tare da nanata iyaye suna kokawa da cewa 'ya'yansu sun bace.

Daga bisani ne kuma Iyayen sabbin sojojin Somalian da aka tura karbar horon suka gudanar da zanga-zanga a birnin Mogadishu inda suka ce gwamnati ta yaudare. su ne da cewar za ta tura ‘ya’yan nasu aiki ne a kasar Qatar, sai kuma kwatsam suka bayyana a kasar Eritrea, inda aka tura su karbar horon soji ba tare da son ransu ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.