Isa ga babban shafi

Mutane sama da 100 sun mutu sakamakon rikicin kabilanci a Sudan

Rikicin da ya barke a yankin Darfur na kasar Sudan tsakanin kungiyoyin Larabawa dasauran kabilu ya yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da 100, kamar yadda hukumomin kasar suka tabbatar.

An samu rarrabuwar kawuna Sudan sakamakon yake yaken basasa.
An samu rarrabuwar kawuna Sudan sakamakon yake yaken basasa. AFP
Talla

Hashem ya ce an kashe mutanen ne mafi yawa a tsakanin kabilar Gimir a lokacin arangamar, amma ba a bayyana adadin mutanen da aka kashe a cikin kabilar Larabawa ba.

Fadan dai ya barke ne a makon da ya gabata bayan wata takaddamar gonaki tsakanin mutane biyu da suka fito daga kabilun biyu..

A cikin watan Afrilu, sama da mutane 200 ne aka kashe a fadan da aka gwabza tsakanin kabilun Larabawa da na Gimir a yammacin Darfur.

Yankin Darfur dai ya kasance cikin yakin basasa a tsawon shekaru uku a lokacin mulkin shugaba Omar al-Bashir.

Yayin da wasu manyan kungiyoyin ‘yan tawaye suka rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a shekarar 2020, har yanzu munanan tashe-tashen hankula na ci gaba da kamari kan rikicin filaye da dabbobi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.