Mutane sama da 100 sun mutu sakamakon rikicin kabilanci a Sudan
Rikicin da ya barke a yankin Darfur na kasar Sudan tsakanin kungiyoyin Larabawa dasauran kabilu ya yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da 100, kamar yadda hukumomin kasar suka tabbatar.
Wallafawa ranar:
Hashem ya ce an kashe mutanen ne mafi yawa a tsakanin kabilar Gimir a lokacin arangamar, amma ba a bayyana adadin mutanen da aka kashe a cikin kabilar Larabawa ba.
Fadan dai ya barke ne a makon da ya gabata bayan wata takaddamar gonaki tsakanin mutane biyu da suka fito daga kabilun biyu..
A cikin watan Afrilu, sama da mutane 200 ne aka kashe a fadan da aka gwabza tsakanin kabilun Larabawa da na Gimir a yammacin Darfur.
Yankin Darfur dai ya kasance cikin yakin basasa a tsawon shekaru uku a lokacin mulkin shugaba Omar al-Bashir.
Yayin da wasu manyan kungiyoyin ‘yan tawaye suka rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a shekarar 2020, har yanzu munanan tashe-tashen hankula na ci gaba da kamari kan rikicin filaye da dabbobi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu