Majalisar Dinkin Duniya ta fara bincike kan cin zarafin fararen hula
Tawagar Majalisar Dinkin Duniya a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ta ce ta fara gudanar da bincike kan rahotannin kashe fararen hula da dama da ake zargin sojojin kasar da kuma sojojin hayar wani kamfanin tsaron Rasha da aikatawa.
Wallafawa ranar:
A cewar wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na AFP ya samu, sojoji da abokan kawancen su, sun kai hari a kauyukan Gordil da Ndah, da ke arewa maso gabashin birnin Bangui, wanda ya yi sanadiyar kashe fararen hula.
Babbar jami'ar Majalisar Dinkin Duniya mai kula da kare hakkin bil'adama, Michelle Bachelet, ta yi Allah wadai da take hakkin bil'adama da aka yi a kasar, da suka hada da kashe ‘yan ba ruwan mu da cin zarafin mata, da kungiyoyin 'yan tawaye da kuma sojojin kasar da kawayensu na Rasha ke aikatawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu