Isa ga babban shafi
madagascar - Ambaliya

Guguwar Batsirai da ta ratsa Madagacar ta hallaka mutum 6

Akalla mutane shida ne suka mutu sakamakon guguwar da akayiwa lakabi da Batsirai mai karfin gaske da ta ratsa kasar Madagascar cikin daren Asabar zuwa Lahadi, lamarin da ya tilastawa mutane kusan 50,000 barin gidajensu tare da fuskantar hadarin ambaliya.

Yadda ambaiyar ruwa ta shafi wasu yankin Madagascar, cikin watan Fabarerun 2022.
Yadda ambaiyar ruwa ta shafi wasu yankin Madagascar, cikin watan Fabarerun 2022. RIJASOLO AFP
Talla

Shugaban hukumar kula da bala'o'i a Madagascar, Paolo Emilio Raholinarivo, cikin wani sako da ya aikewa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya tabbatar da mutuwar mutane 6 sannan wasu kusan dubu 48 suka rasa matsugunansu, amatsayin bayanan wucin gadi.

Hukumomin Madagaska sun nuna cewa karfin guguwar ta ragu, saidai har yanzu akwai fargabar ambaliyar ruwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.