Isa ga babban shafi

Ana zargin dakarun Mali da kisan wasu 'yan kasuwa na Mauritania

A wani kauye mai suna Nara daf da kan iyaka tsakanin Mali da kasar Mauritania, wasu yan kasuwa yan asalin Mauritania 7 ne suka rasa rayukan  su inda ake zargin dakarun kasar Mali da hannu a wannan  kisan wadanan yan kasuwa.

Kan iyaka tsakanin kasar Mali da Mauritania
Kan iyaka tsakanin kasar Mali da Mauritania Christian Aslund/Getty
Talla

Fadar shugaban kasar Mauritania a wata sanarwa mai dauke da sanya hannun shugaban kasar Mohamed Ould Cheikh Ghazouani ta bayyana bacin ran ta,inda shugaban kasar ta Mauritania ya aike da Ministocin harakokin wajen kasar,na tsaro,ministan cikin gida da shugaban hukumar lekken asirin Mauritania  birnin Bamako ,za a gudanar da bincike tare da daukar matakan hukunta mutanen da suka aikata wannan kisa.

Kasuwar birnin  Nouakchott a kasar Mauritania
Kasuwar birnin Nouakchott a kasar Mauritania http://mondoblog.org

Gwamnatin sojin Mali ta shirya don bayar da hadin kanta na ganin  an gudanar da bincike dangane da wannan kisa na yan kasuwar kasar Mauritania.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.