Shugabar Tanzania ta kori wasu daga cikin Ministocin kasar
A Tanzania, Shugabar kasar Samia Suluhu Hassan ta yiwa gwamnatin kwariyar –kwariyar garambawul, sauyin dake zuwa biyo bayan barakar da ake fuskanta a jam’iyyar Chama Cha Mapinduzi dake shugabantar kasar ta Tanzania.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugabar kasar ta salami ministocin shara’a,na gine-gine,masana’antu da kuma zuba jari na kasar ta Tanzania.
Ranar alhamis da ta gabata dai ne Shugaban majalisar dokokkin kasar ta Tanzania Job Ndugai ya sanar da yin murabis,bayan da ya zargin gwamnatin kasar da ciwo bashi daga kasashen waje ba bisa ka’ida ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu