Isa ga babban shafi
Sudan-zanga-zanga

Fararen hula sun jikkata 'yan sanda 58 a zanga-zangar Sudan

Rundunar ‘yan sandan Sudan ta sanar da cewa jami’anta 58 suka jikkata yayin zanga-zangar jiya asabar a birnin Khartoum don kalubalantar mulkin soji a kasar.

Masu zanga-zangar kin jinin gwamnatin Soji a Sudan.
Masu zanga-zangar kin jinin gwamnatin Soji a Sudan. © Marwan Ali, AP
Talla

Yayin zanga-zangar ta jiya jami’an tsaro sun yi amfani da hayaki mai sanya hawaye don hana fararen hula afkawa motoci da gine-ginen jami’an tsaro don nuna fushinsu ga gwamnati.

Rundunar ‘yan sandan ta ce yayin zanga-zangar sun kame mutane 114 kuma za su gurfanar da su gaban kotu don amsa laifukan da suka aikata.

Majiyar ma’aikatar Lafiya a Sudan ta ce fararen hula 178 sun jikkata yayin zanga-zangar wadanda kuma galibi suka samu raunuka sanadiyyar duka ko kuma nuna musu karfi da jami’an tsraon kasar suka yi ciki har da mutum 8 da aka harba a makasa.

Haka zalika majiyar ta ce akwai kuma wasu mutum 48 da suka mutu a hannun jami’an tsaron yayin zanga-zangar galibinsu ta hanyar harbi ko kuma duka a makasa.

Wasu bayanai sun nuna cewa yayin zanga-zangar ta jiya Asabar, hukumomin Sudan sun katse layukan sadarwa ta yadda suka ci karensu babu babbaka kan fararen hula.

Zanga-zangar ta Sudan ta sake kazanta ne bayan mayar da Abdallah Hamdok kan karagar mulki a watan Nuwamba biyo bayan wata yarjejeniya da fararen hulan ke kallo a matsayin wadda bata karbu ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.