Isa ga babban shafi
Sudan

An tarwatsa masu zanga-zangar adawa da sojin Sudan

Dubban masu zanga-zanga sun yi tattaki a yau Asabar a Sudan, watanni biyu bayan sojojin kasar sun yi juyin mulki.

Yadda sojoji suka tarwatsa masu zanga-zangar adawa da su a Sudan.
Yadda sojoji suka tarwatsa masu zanga-zangar adawa da su a Sudan. - AFP/File
Talla

Masu zanga-zangar na bukatar sojojin kasar da su gaggauta komawa barkokinsu, inda kuma suke son a mayar da cikakken karfin iko ga farar hula.

Masu zanga-zangar da ke rike da tutocin kasar, sun yi ta kada manyan gauguna tare da raye-raye da wake-wake a babban birnin Khartoum duk da cewa, an jibge jami’an tsaro masu tarin yawa.

Kodayake daga bisani rahotanni sun ce, jami’an tsaron sun yi amfani da hayaki mai sa-kwalla wajen tarwatsa dandazon masu zanga-zangar.

Akalla mutane 48 ne suka rasa rayukansu a tsawon makwannin da aka kwashe ana gudanar da zanga-zanga a Sudan kamar yadda wata kungiyar Likitocin Kasar ta bayyana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.