Isa ga babban shafi
Lesotho

Tsohon Firaministan Lesotho ya gurfana gaban kotu kan zargin kisan Matarsa

Hukumomin Lesotho sun gurfanar da tsohon Firaministan kasar Thomas Thabane yau a kotun Maseru inda ake tuhumar sa da laifin kashe matar sa Lipolelo.

Tsohon Firaministan kasar Lesotho Thomas Thabane da maidakinsa
Tsohon Firaministan kasar Lesotho Thomas Thabane da maidakinsa Photo: Samson Motikoe/AFP
Talla

Ana zargin Thabane mai shekaru 82 da daukar sojojin haya domin kashe Lipolelo a watan Yunin shekarar 2017, kwana biyu kafin rantsar da shi a matsayin Firaminista.

Akawun kotun Tebello Mokhoema ya karanta tuhume tuhumen da ake yiwa tsohon Firaministan da suka hada da daukar sojojin hayar domin hallaka Lipolelo Thabane a ranar 14 ga watan Yunin shekarar 2017.

Daga cikin mutane 5 da ake tuhuma da aikata kisan akwai amaryar sa Maesaiah wadda aka bada belin ta a watan Yuni, yayinda sauran 4 kuma 'yan bindigar da suka aikata kisan ne.

Rahotanni sun ce tsohon Firaministan da matar da aka kashe sun kwashe dogon lokaci suna rikici a tsakanin su, abinda ya kaiga neman bukatar saki a kotu.

‘Yan Sanda sun ce Thabane ya biya sojojin hayar dala dubu 24 domin kashe matar ta sa, kisan da ya yi sanadiyar raba shi da mukamin sa a watan Mayun shekarar 2020.

Tsohon Firaministan da amaryar sa sun ki amincewa da aikata laifin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.