Lesotho ta zama kasar Afrika ta karshe da annobar COVID-19 ta bulla cikinta
Lesotho ta sanar da bullar cutar coronavirus cikinta, kasar da a baya ta kasance guda daya tilo a nahiyar Afrika da annobar bata shafa ba.
Wallafawa ranar:
Ma’aikatar lafiyar kasar tace wanda aka gano yana dauke da cutar na daga cikin ‘yan kasar 81 da suka koma gida daga kasashen Saudiya da kuma Afrika ta Kudu a makon jiya, aka koma yi musu gwajin cutar.
A ranar 29 ga watan Maris da ya gabata Lesotho ta rufe iyakokinta daga shiga ko fita, domin kare kanta daga bullar annobar ta COVID-19, musamman daga makwafciyarta Afrika ta Kudu.
A wani labarin kuma a kasar ta Lesotho, Fira Ministan kasar Thomas Thabane ya bayyana 22 ga watan Mayun da muke ciki, a matsayin ranar da zai yi murabus.
Masu bibiyar lamurran kasar ta Lesotho na ganin matakin Fira Minista Thabane zai kawo karshen matsalolin da kasar ta shafe akalla watanni 6 tana fama dasu, ciki harda rikicin siyasa, da kuma tsamin dangantaka tsakanin bangaren zartaswa da sojojin kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu