Isa ga babban shafi
Habasha - Tigray

Kungiyar kare hakkin dan adam na zargin 'yan tawayen Tigray da laifukan yaki

Kungiyar kare hakkin dan adam ta Human Rights Watch ta ce sojojin Eritrea da ‘yan tawayen Tigray sun aikata muggan laifukan da suka hada da fyade  kisan gilla, da kuma azabatar da 'yan gudun hijirar Eritrea a yankin Tigray da ke arewacin Habasha, yayin hare-haren da masu rajin kare hakkin dan adam suka bayyana a matsayin laifukan yaki.

Wasu maykan 'yan tawayen Tigray.
Wasu maykan 'yan tawayen Tigray. AFP - YASUYOSHI CHIBA
Talla

Rahoton da Human Rights Watch ta fitar a ranar Alhamis ya ce dakarun na Eritrea da ‘yan tawayen TPLF sun aikata laifukan yakin ne yayin hare -hare da suka kai kan wasu sansanonin ‘yan gudun hijira biyu a yankin Tigray.

Kawo yanzu dai Eritrea ba ta ce komai kan zargin da ake yiwa dakarun na ta ba, sai dai a baya ta sha musanta irin wannan tuhuma kan sojojin nata, kan cin zarafin fararen hula.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.