Isa ga babban shafi

Abiy Ahmad ya bukaci 'yan Habasha majiya karfi da su gaggauta shiga aikin soji

Firaministan Habasha Abiy Ahmad ya bukaci al’ummar kasar majiya karfi da su gaggauta shiga aikin soji saboda kazancewar yakin dake gudana a yankunan kasar guda biyu sakamakon daukar makaman da Yan tawaye suka yi suna yakar gwamnati.

Yara kanana da lamarin yakin Tigray ya ritsa da su
Yara kanana da lamarin yakin Tigray ya ritsa da su © RFI/ Sébastien Németh
Talla

Yanzu ne lokacin da ya kamata daukaci wani balagage Dan Habasha "ya shiga aikin soji  da kuma sojin sa kai domin tabbatar da kishin kasa a cewar pm kasar ta Habasha Abiy Ahmed, watanni 2 bayan da ya ayyana tsagaita buda wuta.

Wani sanssani da aka jibge wasu yan gudun hijira a Habasha
Wani sanssani da aka jibge wasu yan gudun hijira a Habasha © RFI / Sébastien Németh

Tun karshen watan yunin wannan shekara rikicin yankin Tigre ya sake fadawa cikin wani mummunan matsayi da ya kai ga tabarbarewar lamuran jinkai a yankin.

An fara gwabza fada ne a watan novemba shekarar da ta gabata bayan da pm Abiy Ahmed ya aika da sojoji a yankin na Tigre domin kawar da gwamnatin yankin, karkashin kungiyar awaren yankin Tigré (TPLF).

A cewar pm da ya taba lashe lambar zaman lafiya ta  Nobel a 2019, hare haren an kaddamar da su ne a matsayin ramuwar gayya kan harin da yan awaren yankin na tigre TPLF suka kai kan sansanonin dakarun sojin tarayyar kasar.

Yakin yankin Tigray ya tilastawa mutane tserewa daga yankunan su
Yakin yankin Tigray ya tilastawa mutane tserewa daga yankunan su © RFI/Sébastien Nemeth

A karshen watan Nobembar ne kuma Abiy Ahmed ya shelanta samun nasara a fadan bayan da sojin gwamnatin kasar suka sake kwace Mekele babban birnin yankin.

 

To sai dai a ranar  28 ga watan juin, mayakan kungiyar yan tawayen -TPLF sun sake kwace birnin na  Mekele, tare da kwace  mafi yawan yankin na du Tigré a wan safeken.

Bayan tsagaita buda wutar da pm Abiy Ahmed ya kaddamar saboda dalilan jinkai  -da kuma janyewar dakarun na  habasha daga yankin, dakarun yan tawayen na tigre na ci gaba da kai hare hare a kan yankunan yankuna 2 dake makwaftaka da juna na 'Amhara, dake kudanci da 'Afar, dake gabashin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.