Isa ga babban shafi
Namibia - Jamus

Namibia ta yi watsi da diyyar Jamus kan kisan kiyashin mulkin mallaka

Sarakunan gargajiyar Namibia sun yi watsi da neman afuwar da Jamus ta yi gami da alkawarin biyansu diyyar akalla euro biliyan 1, saboda kisan kiyashin da dakarunta suka yiwa dubban jama’a a kasar a zamanin mulkin mallaka.

Wasu fursunoni cikin sarka a Namibia. An dauki wannan hoto a tsakanin shekarun 1904-1908, yayin yakin da aka gwabza tsakanin dakarun Jamus da mayakan kabilun Herero da Nama.
Wasu fursunoni cikin sarka a Namibia. An dauki wannan hoto a tsakanin shekarun 1904-1908, yayin yakin da aka gwabza tsakanin dakarun Jamus da mayakan kabilun Herero da Nama. © National Archives of Namibia/AFP via Getty Images
Talla

A cewar Sarakunan gargajiyar da suka fito daga kabilar Nama da Herero, euro biliyan daya bai isa diyyar kisan kare dangin da Jamusawan mulkin mallakar suka yi musu ba.

Matakin dai ya zo ne kwana guda bayan da a ranar Juma’a gwamnatin Jamus ta amince da aikata kisan kare dangi a Namibia a lokacin mulkin mallaka.

Turawan mulkin mallaka na Jamus sun kashe dubun dubatan kabilun ‘yan asalin Herero da Nama a wani kisan gillar da aka yi a shekarun 1904-1908 - wanda masana tarihi sukayi wa lakabi da kisan kare dangi na farko a karni na 20 da ya lalata dangantaka tsakanin Namibia da Jamus tsawon shekaru.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.