Isa ga babban shafi
Habasha-Eritrea

EU ta bukaci gaggauta ficewar dakarun Eritrea daga yankin Tigray

Kungiyar Tarayyar Turai ta bukaci sojojin Eritrea da su gaggauta ficewa daga 'yankin da ake samun tashin hankali a Tigray na kasar Habasha kamar yadda ta yi alkawari.

Wasu dakarun Sojin Habasha da ke aiki da na Eritrea wajen tabbatar da zaman lafiyar yankin Tigray da ya yi fama da rikici.
Wasu dakarun Sojin Habasha da ke aiki da na Eritrea wajen tabbatar da zaman lafiyar yankin Tigray da ya yi fama da rikici. France24
Talla

Babban jami’in diflomasiyar kasashen Turai Josep Borrell ya ce ba a samun cigaban kirki a yankin Tigray, yayin da ake cigaba da gwabza fada da kuma fama da matsalolin ayyukan jinkai.

Jami’in ya shaidawa ministocin harkokin wajen Turai cewar Eritrea ta amince da rawar da ta taka a Tigray, yayin da ta yi alkawarin janye dakarunta daga cikin Habasha.

An dai kwashe watanni gwamnatin Habasha da takwararta ta Eritrea na musanta cewar dakarun Eritrea na cikin kasar a yankin na Tigray da ya yi fama da rikici.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.