Ghana tayi bikin cika shekaru 64 da samun 'yancin kai daga Birtaniya
Kasar Ghana tayi bikin cika shekaru 64 da samun ‘yancin kai daga Turawan mulkin mallakar Ingila, sakamakon zaman kasar ta farko a Afirka da tayi watsi da mulkin mallaka a ranar 6 ga watan Maris na shekarar 1957.
Wallafawa ranar:
Kamar yadda aka saba yau an gudanar da shagulgula da faretin soji domin tuna irin gwagwarmayar da shugabannin farkon suka yi na ganin kasar ta samu ‘yancin cin gashin kai.
A sakon shugaba Nana Akufo-Addo ga al’ummar kasar ya jinjinawa shugabannin Ghana na farko da suka budewa kasashen Afirka kofar samun yancin a matsayin kasa ta farko da kuma cigaba da rike tuta wajen tabbatar da cewar kowacce kasa a Afirka ta samu ‘yanci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu