Isa ga babban shafi

Mutane dubu 7 sun bar yankin Tigray na Habasaha zuwa Sudan-MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutane kusan dubu 7 suka tserewa gidajen su zuwa kasar Sudan domin kaucewa yakin da aka fafata tsakanin sojojin gwamnatin Habasha da 'yan Tawayen yankin Tigray.

Wasu daga cikin mazauna yankin Tigray da suka tserewa rikici, yayin da suke dakon karbar tallafi a sansanin 'yan gudun hijira na Um-Rakoba dake kan iyakar Sudan da Habasha. 17/12/ 2020.
Wasu daga cikin mazauna yankin Tigray da suka tserewa rikici, yayin da suke dakon karbar tallafi a sansanin 'yan gudun hijira na Um-Rakoba dake kan iyakar Sudan da Habasha. 17/12/ 2020. REUTERS/Mohamed Nureldin Abdallah
Talla

Hukumar agajin gaggawa ta Majalisar ta ce matsalar ta biyo bayan rikicin da aka samu tsakanin bangarorin biyu wanda ya gamu da suka daga sassan duniya.

Kakakin hukumar Babar Baloch ya ce matsalar yankin ya yi kamari a cikin watanni 3 da suka gabata.

Ko a baya-bayan nan sai da Majalisar ta yi gargadi kan yadda yunwa ke barazana ga yankin na Tigray da har yanzu ke fama da burbushin rikici da kuma mamayar Sojin Habasha.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.