Isa ga babban shafi
Habasha

Yunwa na barazanar halaka dubban mutane a yankin Tigray - MDD

Majalisar dinkin duniya ta bayyana damuwa kan yadda yunwa ke karuwa a yankin Tigray mai fama da rikici a kasar Habasha.

Wasu daga cikin mazauna yankin Tigray da suka tserewa rikici, yayin da suke dakon karbar tallafi a sansanin 'yan gudun hijira na Um-Rakoba dake kan iyakar Sudan da Habasha. 17/12/ 2020.
Wasu daga cikin mazauna yankin Tigray da suka tserewa rikici, yayin da suke dakon karbar tallafi a sansanin 'yan gudun hijira na Um-Rakoba dake kan iyakar Sudan da Habasha. 17/12/ 2020. REUTERS/Mohamed Nureldin Abdallah
Talla

Cikin sabon rahoton da ta wallafa, majalisar dinkin duniyar ta bayyana fadan da ake cigaba da gwabzawa tsakanin dakarun Habasha da ‘yan tawayen TPLF, da matsalar Diflomasiya da kuma katsalandan din wasu kasashen ketare, a matsayin batutuwan dake kara tagayyara al’ummar yankin na Tigray da rikici ya daidaita.

Rahoton ya kara da cewa, kwanaki sama da 100 bayan barkewar yaki a yankin Tigray, har yanzu jami’an agaji sun kasa isa ga mazauna yankunan karkara masu yawan gaske.

A farkon watan Fabarairu kungiyar bada agaji ta kasa da kasa Red Cross tayi gargadin cewa yunwa za ta halaka dubban mutane a yankin an Tigray, muddin aka cigaba da hana jami’an agaji gudanar da ayyukansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.