Isa ga babban shafi
Habasha

MDD na fargaba kan yaduwar annobar coronavirus a yankin Tigray

Majalisar dinkin duniya ta bayyana fargaba kan yiwuwar fuskantar yaduwar annobar coronavirus a yankin Tigray mai fama da rikici a kasar Habasha.

Wasu daga cikin dubban 'yan gudun hijirar da suka tserewa rikicin yankin Tigray zuwa cikin Sudan.
Wasu daga cikin dubban 'yan gudun hijirar da suka tserewa rikicin yankin Tigray zuwa cikin Sudan. AP Photo/Nariman El-Mofty, File
Talla

Gargadin na kunshe cikin wani rahoto da majalisar ta wallafa a karshen makon nan kan fadan da ake gabzawa tsakanin dakarun gwamnati da ‘yan tawayen TPLF a yankin na Tigray, wanda ya dubban mutane da muhallansu, gami da rushewar asibitoci da sauran cibiyoyin kula da lafiya.

Sai dai tsawon akalla watanni 2 bayan barkewar rikicin, jami’an agaji sun samu damar fara ayyukan jin kai a yankin.

Rikicin yankin na Tigray dai yayi barazanar zama babban kalubale ga Habsha kasa ta biyu mafi yawan jama’a a Afrika, zalika tuni rikicin ya soma shafar makwabtan kasar da suka hada da Sudan, da kuma Eritrea.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.