Isa ga babban shafi
Ghana

Ghana ta zarta kasashen yammacin Afrika wajen yawan masu corona

Hukumar lafiya ta duniya tace Ghana ta zama kasar dake kan gaba wajen yawan masu cutar coronavirus a yammacin nahiyar Afrika.

Wani jami'in tsaro a Ghana, sanye da takunkumin rufe fuska don samun kariya daga cutar coronavirus.
Wani jami'in tsaro a Ghana, sanye da takunkumin rufe fuska don samun kariya daga cutar coronavirus. REUTERS/Francis Kokoroko
Talla

Alklaumman hukumar ta WHO sun nuna cewa yanzu haka jumillar mutane dubu 4 da 263 ne suka kamu da cutar a Ghana, yayinda wasu 2 suka mutu, 378 kuma suka warke.

Hukumar lafiyar tace a rana guda, mutane 921 suka kamu da cutar ta COVID-19 a Ghana, kasa da kwanaki 20 bayan janye dokar hana fita a manyan yankunan kasar na Accra da Kumasi da shugaba Nana Akufo Addo yayi.

A baya Najeriya ke kan gaba wajen yawan masu cutar ta corona a yammacin Nahiyar Afrika, amma hauhawar adadin na Ghana ya maida ta mataki na 2.

Zuwa lokacin wallafa wanna labari Afrika ta Kudu ke kan gaba a nahiyar Afrika baki daya, wajen yawan mutanen da suka kamu da cutar coronavirus da adadin dubu 8 da 895, sai Algeria mai mutane dubu 5 da 369, Ghana dubu 4 da 263, Najeriya dubu 4 da 151, yayinda Kamaru ke da jumillar mutane dubu 2 da 274.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.