Likitocin Ghana 13 sun kamu da cutar coronavirus
Kungiyar likitocin kasar Ghana tace akalla manbobinta 13 sun kamu da cutar coronavirus.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaban reshen kungiyar likitocin ta GMA na yankin Ashanti, Paa Baidoo ne ya sanar da kamuwar likitocin a yau talata.
Dakta Baidoo ya dora alhakin aukuwar lamarin kan rashin isassun kyayyakin baiwa likitoci kariya daga kamuwa da cutar ta COVID-19.
Zuwa ranar talatar nan 28 ga watan Afrilu, yankin Ashanti ke kan gaba a kasar Ghana wajen yawan wadanda da suka kamu da cutar coronavirus, da adadin mutane 69.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu