Isa ga babban shafi
Zimbabawe

Farashin litar mai daya ya haura naira dubu a Zimbabwe

Shugaban Zimbabwe, Emmerson Manangagwa ya sanar da karin farashin litar man fetur da sauran albarkatunsa.

Shugaban kasar Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa.
Shugaban kasar Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa. REUTERS/Philimon Bulawayo
Talla

Manangagwa ya ce matakin ya zama tilas domin kawo karshen karancin man da kasar ke fuskanta, mafi muni da suka taba fuskanta cikin shekaru 10.

A lokacin da yake sanar da matakin a jiya Asabar, shugaban na Zimbabwe, ya ce farashin litar mai ya koma dala uku da doriya, kwatankwacin naira dubu 1 da 200, daga dala daya, wato dai dai da naira 350.

Matakin kara farashin albarkatun man da gwamnatin Zimbabwe ta dauka, ya zo ne bayan da ta sha alwashin samar da wani sabon kudin kasar cikin shekara daya, domin kawo karshen matsalar tattalin arzikin da take fuskanta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.