Isa ga babban shafi

Akwai jahilai fiye da miliyan 60 a Najeriya

Ma’aikatar ilimi a Najeriya ta yi ikirarin cewa kasar na da tarin jahilai akalla miliyan 60 da suka kunshi matasa maza da mata da kuma wadanda shekarunsu ke da yawa.

Kashi 60 cikin 100 na adadin jahilan da Najeriya ke da su mata ne, galibi kuma kananan yara.
Kashi 60 cikin 100 na adadin jahilan da Najeriya ke da su mata ne, galibi kuma kananan yara. AFP/BOUREIMA HAMA
Talla

A jawabin da ya gabatar yayin taron ranar yaki da jahilci ta duniya, ministan ilimi na Najeriyar Malam Adamu Adamu ya ce akwai akalla yara miliyan 11 da basa zuwa makaranta a kasar.

Malam Adamu Adamu wanda ya samu wakilcin Mr Prinzo James mataimakin daraktan sashen kula da ilimin Firamare da Sakandire na Najeriyar, ya ce daga cikin adadin jahilan da suka gano kashi 60 cikin dari mata ne matasa.

A jawaban na sa, Adamu Adamu ya ce an samu raguwar jahilan da kasar ke da su bayan samar da makarantun yaki da jahilci da ya tilastawa dattijai da dama komawa karatu yayinda ya bukaci daukar mataki don kawar da jahilci a Najeriyar.

Malam Adamu Adamu ya ce akwai bukatar daukar kwararan matakai don kawar da matsalar jahilci a tsakanin al’ummar kasar nan da shekarar 2030, dalili kenan da ya sanya Gwamnatin kasar fara shirye-shiryen gabatar da wani shirin yaki da zalunci a ilahirin sassan kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.