Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Congo

Cutar Ebola ta tafka barna a Jamhuriyar Congo - WHO

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta bayyana annobar cutar Ebola da ta sake barkewa a Jamhuriyar Congo a matsayin wadda ke mataki na biyu mafi muni a tarihi, bayan annobar cutar da ta hallaka dubban jama’a a Afrika ta Yamma cikin shekarun baya.

Wasu wurare  da aka ware domin killacewa da kuma kula da wadanda suka kamu da cutar Ebola.
Wasu wurare da aka ware domin killacewa da kuma kula da wadanda suka kamu da cutar Ebola. RFI/Florence Morice
Talla

Rahoton na zuwa ne a dai dai lokacin da ma’aikatar lafiyar jamhuriyar Congo ta sanar da cewa, yawan wadanda suka kamu da cutar ta Ebola a baya bayan nan ya kai 426.

Kawo yanzu dai ma’aikatar lafiyar ta Congo, tace mutane 198 cutar ebolan ta hallaka, tun bayan sake bullarta a ranar 1 ga watan Agustan da ya gabata.

Cutar dai tafi shafar garin Beni dake gabashin kasar, da kuma lardin Kivu a arewaci, wadanda ke fama da hare-haren kungiyoyin mayaka, lamarin da ya dakle kokarin jami’an lafiya wajen magance yaduwar cutar a yankunan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.