Jamhuriyar Congo ta amince da gwajin maganin Ebola kan jama'arta
Jamhuriyyar Dimokiradiyar Congo ta amince da yin gwajin maganin cutar Ebola kan wasu yan kasar da suka kamu da cutar, domin bai wa masanan kimiyya damar tattara bayanai game da sahihancin maganin.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce tuni ma’aiakatan lafiya suka yi wa mutane sama da 150 gwajin maganin tun daga watan Agusta domin magance yaduwar cutar.
Ma’aikatar lafiyar kasar ta ce bayanan da za’a tatatra daga gwajin maganin zai ba da damar inganta shi domin ceto rayukan Bil Adama.
Hukumar lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutane 228 suka mutu tun barkewar cutar watanni 6 da suka gabata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu