Rundunar sojin saman Najeriya ta aike da jirage Zamfara
Rundunar sojin saman Najeriya ta aike da karin jirage biyu ga rundunarta da ke aikin wanzar da zaman lafiya a jihar zamfara karkashin shirin kai daukin gaggawa ga yankunan da ke fuskantar barazanar tsaro a jihar Zamfara.Matakin rundunar na zuwa ne a dai dai lokacin da yawan ‘yan gudun hijira da suka kauracewa kauyukansu sakamakon matsalar tsaro a sassan jihar ta Zamfara ke tasamma dubu 10.
Wallafawa ranar:
Kwamandan rundunar 207 da ke yaki da ayyukan ta’addancin a Zamfara Kaftin Caleb Olayera ta hanyar aiki da jiragen Shalkwaftar ne za a iya kai daukin gaggawa ga yankunan da ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga.
A cewar kwamandan maimakon jiran karin dakaru daga jihohin Kano da Bauchi yanzu jiragensu za su fara tashi daga birnin Gusau don kai dauki a sassan da ke cikin matsala ta hanyar shawagi a sararin samaniya.
Rundunar dai ta samu karin akalla jirage biyu daga shalkwatarta ta kasa don fatattakar ‘yan bindigar da ke barazana ga rayuka da dukiyoyin al’umma a jihar ta Zamfara.
Yanzu haka dai dubban al’ummar jihar ta Zamfara mazauna kauyuka wadanda suka samu tsira da rayukansu daga hare-haren ‘yanbindigar na ci gaba da samun mafaka a biranen jihar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu