An ceto baki kusan 400 a saharar Nijar
Hukumar Kula da kaurar jama'a ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce, akalla baki kusan 400 'yan Afirka aka ceto a tsakiyar sahara bayan sun fada cikin halin kuncin na rashin abinci da ruwan sha a makon jiya.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Sanarwar hukumar ta ce, mutane 386 daga kasashe 3 sun shiga tsaka mai wuya ne tsakanin yankin Arlit da Assamaka da ke kusa da iyakar Algeria akan hanyarsu ta zuwa Turai.
Hukumar ba ta sanar da kasashen da bakin suka fito ba da kuma dalilin da ya jefa su cikin halin da suka samu kan su a ciki ba, sai dai ta ce, yanzu haka daukacin mutanen na samun mafaka a wani da ke Arlit, in da ake kula da su.
Hukumar ta ce, a cikin wannan shekara ta kai irin wannan dauki har sau 18, in da ta ceto ire-iren wadannan baki kusan 3,000.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu