Isa ga babban shafi
Nijar

'Yan Mali sama da dubu 8 sun tsallaka cikin Nijar

Majalisar Dinkin Duniya ta ce, akalla 'yan kasar Mali sama da dubu 8 suka tsallaka Tilaberi da ke Jamhuriyar Nijar domin kauce wa tashin hankalin da ake samu na hare haren 'yan ta’adda.

Hare-haren 'yan bindiga sun tilasta wa mutane fice daga Mali zuwa Nijar
Hare-haren 'yan bindiga sun tilasta wa mutane fice daga Mali zuwa Nijar REUTERS/Paul Carsten
Talla

Ofishin Jinkai na Majalisar yace,  daga watan Janairu zuwa yanzu, mutanen da suka rasa matsugunansu sun kai dubu 8 da 432 sakamakon hare -haren da yan ta’adda ke kaiwa.

Majalisar tayi gargadin cewar adadin na iya tashi zuwa dubu  40 ganin yadda yankin ke dauke da wasu 'yan gudun hijira daga Mali tun bayan barkewar tashin hankali a shekarar 2012.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.