Isa ga babban shafi

Rundunar Faransa ta kashe 'yan ta’adda a kan iyakar Mali da Algeria

Rundunar Sojin Faransa ta sanar da kashe wasu ‘yan ta’adda 15 a kan iyakar Mali da Algeria a ci gaba da farautar masu ta da kayar baya a Yankin.

Dakarun da ke aikin wanzar da zaman lafiya a Mali
Dakarun da ke aikin wanzar da zaman lafiya a Mali STRINGER / AFP
Talla

Mai Magana da yawun ma’aikatar tsaron Faransa ya ce an kai harin ne daren litinin a Yankin Abeibara kan ‘ya’yan kungiyar Ansaruddine.

Bayanai sun ce anyi amfani da jiragen saman yaki da jirage masu saukar ungulu da kuma sojojin kasa wajen kai harin.

Babu dai Karin haske ko harin na da nasaba da kisan da aka yiwa sojojin Amurka da Nijar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.