Isa ga babban shafi
DR Congo

Tshisekedi Madugun adawar Congo ya rasu

Tsohon Firaministan Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo, kuma shugaban madugun adawar kasar Etienne Tshisekedi ya rasu a wani asibitin Brussels yana da shekaru 84 a duniya.Tshisekedi ya taka gagarumar rawa wajen yaki da mulkin kama karya a Congo tun lokacin mulkin shugaba Mobuto Sese Seko.

Shugaban 'Yan adawar Jamhuriyyar Congo Etienne Tshisekedi
Shugaban 'Yan adawar Jamhuriyyar Congo Etienne Tshisekedi REUTERS/Kenny Katombe
Talla

Tun zamanin mulkin Mobutu Sese Seko, Tshisekedi ke gwagwarmayar tabbatar da dimokuradiya a Congo.

Ya rike mukamin Firaminista a karkashin Gwamnatin shugaba Mobuto Sese Seko har sau hudu, ya taka gagarumar rawa wajen yaki da mulkin kama karya a tarihin Congo, da ta yi fama da yakin basasa da juyin mulki da kuma mulkin kama karya.

Ya fara zama minista a karkashin gwamnatin Mobuto kafin ya taimaka wajen kafa Jam’iyyar UDPS a shekarar 1982 lokacin da ake kiran kasar Zaire.

Sau hudu Mobuto na nada shi Firaminista a shekarar 1990 amma kuma ba ya wuce watanni, saboda yadda manufofinsa ke karo da na shugaba Mobuto.

Tshisekedi ya yi gwagwarmaya da shugaba Laurent kabila a shekarar 1997 da kuma dansa wanda ya hau karagar mullki a shekarar 2001.

A tattaunawar neman warware rikicin siyasar kasar, an sake shirya ba shi mukamin Firaminista dan shirya yadda shugaba kabila zai bar mulki a wannan shekarar, kafin tafiyarsa Belguim dan duba lafiyarsa, kuma a can Allah Ya karbi ran sa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.