Isa ga babban shafi
Gambia

Sabon Shugaban Gambia ya cire Kalmar Islam daga jerin sunan kasar

Sabon Shugaban kasar Gambia Adama Barrow ya tsame Kalmar 'Islama'  daga cikin sunan da ake kiran kasar ta su.

Sabon shugaban Gambia Adama Barrow
Sabon shugaban Gambia Adama Barrow REUTERS/Thierry Gouegnon
Talla

A tattaunawa da manema labarai karon farko Adama Barrow ya kuma ce za'ayi sauye-sauye sosai wajen harkokin tsaron kasar, yayinda  ‘yan jaridu za su sami ‘yancin walwala sosai.

Ya ce zai sauya sunan Hukumar tsaron kasar, wadda ta kunshi ‘yan sandan  da ake jin tsoro saboda karfin iko da aka basu.

A shekara ta 2015 ne dai tsohon shugaba Yahya Jammeh ya sauya yadda ake kiran sunan Gambia ta zama janhuriyar Islama ta Gambia

Kashi 90% daga cikin mutan kasar dai musulmi ne.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.